XtGem Forum catalog
Uzairu badamasi

BARKA DA ZUWA SHAFI MAI ALBARKA

Alhamdulillah muna muku albishir insha Allah zamu dawo aiki gadan gadan!


Shafin farko

Haidar Ali
An Kashe Jami'an 'Yan Sanda 6 A Arewa Maso Gabashin Najeriya

05 Disamba 2017
yan sd

Hukumar 'yan sandar Najeriya ta sanar da kashe jami'anta shida a wani rikicin manoma da makiya a garin Numan dake jihar Adamawa.

Kamfanin dillancin labaran kasar Faransa ya nakalto hukumomin 'yan sandar Najeriya na cewa wani rikici mai nasaba da kabilanci da kuma rikicin gonaki ya barke a kauyukan da ke kusa da garin Numan, lamarin da ya hana masu tafiya wucewa tare da tilasta wa wasu kauracewa daga garin Numan, kauyukan da aka kai wa hare-haren sun hada da Bono da Laworu da Dom, duka a kusa da garin Numan.

Usman Abubakar kakakin 'yan sandar jihar Adamawa ya bayyana cewa an tura jami'an 'yan sandar ne domin kwantar da tarzoma tare kuma da kwace makaman dake a hanun bangarorin biyu, sai rikcin ya ritsa da jami'an 'yan sandar guda shida.

Rahoton ya ce har yanzu babu wani mutum da aka kame a wannan rikici, a cikin 'yan kwanakin nan rikicin tsakanin manoma da makiya na kara tsananta, inda a ranar 20 ga watan Nuwambar da ya gabata, irin wani rikici ya lashe rayukan mutane 20 tare da jikkata wasu 30 na daban.


.
Copyright © 2018~2022.
( Uzairu Badamasi Sufi )
Harkarmusulunci@yahoo.com
All rights reserved

Bamu Da Alhakin Tallar Da Ake Sawa Akan Wannan Website Din